8 Yuli 2026 - 15:29
Source: ABNA24
Iran: A Martanin Farko Ga Ta'addancin Amurka Ta Kai Hari A Kan Wuraren Soji 85 Na Amurka

Ofishin Hulda da Jama'a na Sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya sanar da cewa: Biyo bayan harin Amurka a kan wuraren soji da na fararen hula a kudancin ƙasar, da kuma keta sassan daga sassa 14 na yarjejeniyar fahimtar juna, tun daga safiyar yau, jiragen mara matuki masu kai hari na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, sun kai hari kan cibiyoyin taron sojojin Amurka a "Sansanin Sheikh Isa" da ke Bahrain.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya bayar da rahoton cewa: Sakamakon keta da karya tsagaita wuta a fili da maimaituwar hakan daga Amurka yar ta’adda, dukkan sansanonin Amurka a yankin sun zama halstattun hadafin hari ga jiragen marasa matuki na sojojin Iran.

Dakarun Juyin Musulunci na Iran sun sanar da cewa, a martani na farko ga ta'addancin Amurka na yau, sojojin ruwa da sararin samaniya na dakarun juyin musulunci, a wani aiki na hadin gwiwa na makamai masu linzami da jiragen mara matuki, sun markade wurare 85  na muhimman cibiyoyin soji na Amurka, kuma sun harbo wani jirgin mara matuki na MQ9 sa sararin samaniyar kasar a yankin Bushehr.

Biyo bayan jarumtar al'ummar Iran mai girma a jana'izar jagora shahidin al'ummar Musulunci da ta karya ƙarfin makiya da ba a taɓa yin irinta ba a wannan zamanin, gwamnatin Amurka mai ta'addanci wadda girman rashin nasararta ke bayyana kowace rana, yayin da take ganin martanin duniya na yunkuri mai girma na al'ummar Iraki mai daraja a rakiyar jagora mujahidi shahidi a matsayin babbar rashin nasara a gare ta, ta sake maimaita halyyarta ta karya alkawari, cikin firgici don rufe wannan lamari na tarihi, sojojin Amurka masu kashe yara da ta'addanci a farkon sa'o'in safiyar yau, ta hanyar harin sama a kan wasu sansanonin bakin teku da wuraren fararen hula a gabar tekun lardin Hormozgan da Mahshahr, sun keta tsagaita wuta a fili, kuma sun lalata fahimtar juna ta Islamabad.

A martani na farko ga wannan ta'addanci, sojojin ruwa da sararin samaniya na dakarun juyin musulunci na Iran, a wani aiki na hadin gwiwa na makamai masu linzami da jiragen mara matuki, sun murkushe wurare 85 na muhimman cibiyoyin soji na Amurka a tashar jiragen ruwa ta Salman, yanki na biyar na ruwa na Bahrain, da sansanin sojan sama na Ali al-Salem na Kuwait, kuma sun harbo wani jirgin mara matuki na MQ9 na makiya wanda ke da niyyar shiga cikin aikin.

.......................

Your Comment

You are replying to: .
captcha